in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jama'ar yankin gabas ta tsakiya suna da ikon tabbatar da makomar yankinsu, a cewar Yang Jiechi
2012-03-06 15:12:50 cri

A ran 6 ga wata a nan birnin Beijing, ministan harkokin waje na kasar Sin Yang Jiechi ya bayyana cewa, ana samun babban canji a yankin gabas ta tsakiya, amma jama'ar yankin sun san halin da ake ciki a yankin sosai, sabo da haka, kamata ya yi jama'ar yankin su warware matsalolin yankin da kansu tare da samun ikon tabbatar da makomar yankin.

A gun taron manema labaru na taro na 5 na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 11 da aka gudanar a wannan rana, Yang Jiechi ya bayyana cewa, kasar Sin da wasu kasashen Larabawa suna da bambancin ra'ayoyi kan wasu batutuwa, amma suna da ra'ayi iri daya wajen kiyaye zaman lafiya da samun bunkasuwa a yankin gabas ta tsakiya. Ba za a iya kawo illa ga zumuncin dake tsakanin Sin da kasashen Larabawa ba.

Game da batun Syria, Yang Jiechi ya ce, ra'ayin kasar Sin, musamman jawabin kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin, ya jawo hankalin kasa da kasa sosai, kana an kara samun fahimtar juna da goyon baya daga sauran kasashen duniya.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China