in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta ba da tallafi ga kasashen Turai bayan da suka kara karfinsu na magance rikici
2012-02-27 16:15:27 cri
Ranar Lahadi 26 ga wata, mataimakin ministan kudi na kasar Sin Zhu Guangyao wanda ya halarci taron ministocin kudi da shugabannin bankunan tsakiya na kungiyar G20 da aka yi a birnin Mexico ya shedawa manema labaru cewa, Sin za ta yi hadin gwiwa da kasa da kasa domin ba da taimako ga nahiyar Turai bisa tsarin asusun ba da lamuni na duniya IMF da G20 bayan da wasu kasashen Turai suka yi kokarin kara karfin magance rikicinsu.

Zhu Guangyao ya ce, shugabannin kasar Sin sun jaddada sau da dama cewa, Sin na nuna imani cewa, nahiyar Turai na da karfin warware rikicin kudin Euro da karfin kansu, kuma na da karfin warware kalubalen da take fuskanta.

Wata sabuwa kuma, an rufe taron ministocin kudi da shugabannin bankunan tsakiya na kungiyar G20 a wannan rana, inda aka tattauna kan halin tattalin arzikin da duniya ke ciki, da batun kara daidaita tsarin kudi na duniya da sauransu. Daga bisani kuma aka fitar da wata sanarwa bayan taro, inda ta yi maraba da matakan da kasashen Turai suka dauka wajen daidaita ayyukan kudi, magance kalubalen dake cikin kasuwannin kudi, kyautata tsarin kudi, sa kaimi ga kwaskwarima da aka yi wa tsare tsare da zummar samun bunkasuwa, da kuma ba da taimako ga kasar Girka. Ban da wannan kuma sanarwar ta yi kira da a yi wa tsari kwaskwarima a yankin dake yin amfani da kudin Euro cikin hanzari.

An ba da labarin cewa, tawagar kasar Sin ta halarci taron a karkashin jagorancin shugaban bankin jama'ar kasar Zhou Xiaochuan da mataimakin ministan kudi na kasar Zhu Guangyao.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China