in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a daidaita batun Sham bisa tushen tabbatar da moriyar jama'ar kasar
2012-02-17 11:20:21 cri

Jaridar People's Daily ta bayar da jawabi a ran 17 ga wata cewa, ya kamata a dauki nauyin tabbatar da moriyar jama'ar kasar Sham da zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiya. Kasar Sin tana da matsayinta, kuma ta dauki matakai a kan wannan batu, ya kamata kasashen duniya su daidaita batun kasar Sham bisa wannan tushe.

Bayanin ya bayyana cewa, rikicin kasar Sham ya kawo mummunan tasiri sosai ga jama'ar Sham, kana ya zama kalubale mai tsanani a gaban gamayyar kasa da kasa. Ya kamata a yi Allah wadai da dukkan tashe tashen hankalin da ya rutsa da fararen hula a kasar, kuma dole ne a dakatar da duk wani tashin hankali cikin gaggawa. Don haka, ya kamata gamayyar kasa da kasa ta tsaya kan matsayinta, kuma ta dauki matakai masu yakini.

Ban da haka kuma, bayanin ya ce, ya kamata a kawo karshen rikici cikin gaggawa, kuma ya fi kyau a yi hakuri da juna, daukar matakan soja domin hambarar da gwamnati ba hanya ce da ta dace ba. Idan aka yi kuskuren karya dokar MDD, to batun kasar Sham zai kara tsananta, kuma hulda a tsakanin kasa da kasa za ta lalace.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China