in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Minista a kasar Africa ta Kudu ta fito fili ta fara yakin nema mukami mafi girma na kungiyar tarayya kasashen Africa
2012-01-19 11:08:29 cri
Labarin da kamfanin dillancin labarai ta kasar Sin Xinhua ta ba mu ya nuna cewa yanzu haka dai an tabbatar da Ministar harkokin cikin gida ta kasar Afirka ta Kudu, Nkosazana Dlamini-Zuma, a hukumance tana neman karawa da Jean Ping na kasar Gabon a matsayin Shugaban kungiyar tarayyar kasashen Africa AU.

Kamar yadda gidan radiyon 'Talk Radio 702' a Johannesburg ta yada, a ranar Laraba ne ministan harkokin wajen kasar Afirka ta Kudu Maite Nkoane-Mashabane ya sanar da hakan, ya ce yana da imanin cewa Madam Dlamini-Zuma za ta lashe wannan zaben.

Mambobin kungiyar AU 53 ne za su jefa kuri'a don tabbatar da wannan matsayin a lokacin taronta da za'a yi a Addis Ababa,babban birnin kasar Habasha a karshen watan nan na Janairu.

Gidan rediyon ta ce jami'an kasar Africa ta Kudu suna ta zawarcin sauran mambobi don su goyi bayan Madam Dlamini-Zuma.

Mista Nkoane-Mashabane yace an tsaida shawarar shiga takarar ne a taron kasashe 14 na kungiyar cigaban yankin kasashen kudancin Africa da aka yi a watan Agusta na bara inda Nkosazana Dlamini-Zuma, tsohuwar ministar harkokin wajen kasar Afirka ta Kudu, ta samu goyon baya gaba daya. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China