in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Ghana ta samu karuwar matsayi da hawa 3 a jerin matsayin hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA
2012-01-19 10:17:50 cri
Ghana ta daga da matsayi 3 a jerin matsayin da hukumar kwallon kafa na duniya FIFA ta gabatar a wannan watan Janairu inda ta zama na matsayi 26 a madadin 29 da take da shi a watan jiya,a sanarwar da hukumar kwallon kafa ta kasar Ghana ta yi jiya Laraba.

Kungiyar kwallon kafa ta maza ta kasar Ghana da aka ba ta lakabin Black Stars,wadda ke da niyyar cirar tutar gasar cin kofin Afirka a 2012,ta fara shekarar ne da zama na biyu a nahiyar Africa inda take biye da kasar Cote d'ivoire bayan da ta samu maki 18 a wannan shekara, wanda ya kara da na da ya zama maki 779.

Kasar Aljeriya ita ce na 3 sai kasar Masar na biye a matsayi na 4 a nahiyar baki daya kamar yadda mizanin awon ya nuna.

Zakarun duniya Kasar Spain har yanzu ita ke gaba a matsayi na daya a duniya sai kasar Netherland na biye da ita a matsayin na biyu sai na 3 kuma kasar Jamus.

Babbar hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA na sa ran samun wani canji a watan gobe na Fabrairu, ganin cewa za'a kaddamar da gasanni baki daya 32 a karkashin laimar babbar gasar cin kofin Afirka, wadda za ta fara a ranar 21 ga watan nan da muke ciki.

Kasar Ghana dai ta shiga karon kusa da na karshe a gasar cin kofin duniya da ta gudana a kasar Africa ta Kudu a shekara ta 2010.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China