in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Somalia ta ce sabon shugaban majalisar kasar haramtacce ne
2012-01-06 11:00:21 cri
A cikin wata sanarwa daga hukumomin kasar Somalia, gwamnatin kasar ta bayyana zaben shugaban majalisar dokoki da 'yan majalisar suka gudanar a matsayin wani haramtaccen zabe.

Bugu da kari,gwamnatin ta yi fatali da zaben tare da yi Allah wadai da fadan da ya wakana a majalisar

Taro na musamman da kwamitin tsaro na kasar ya gudanar, tare da halartar shugaban kasar Somalia,da shugaban majalisar da aka soke ,da firaministan kasar, ya amince cewa, tattaunawar da 'yan majalisar kasar suka gudanar haramtacciya ce wadda ba ta da wani tasiri.

A dai taron da aka gudanar a ranar Labara ne fada ya barke a majalisar dokokin kasar,inda aka yi kaca-kaca da ginin majalisar kasar da kuma lalata wasu abubuwa ,abun da gwamnati ta yi Allah wadai a kai.

Gwamnati ta dauki matakan hana sake abkuwar irin wannan lamari tare da matakan gaggauta kammala sabon kudin tsarin mulki na kasa,da gudanar da zaben 'yan majalisar kasar kamar yadda taron tattaunawa na MDD na baya-baya da ya gudana a Mogadishu ya amince.

Kwamitin tsaro na kasar na yankin kohon Afirka ya umarci dukkan mambobin majalisar da su darajanta tsarin tarraya na rikon kwarya da ya kasance ginshikin dokokin kasar. (Abdou Halilou)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China