in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afrika na bukatar a kalla dala biliyan 500 domin tinkarar batun sauyin yanayi
2011-12-01 15:30:29 cri
Ranar Laraba 30 ga watan Nuwanba a gun taron Durban, kungiyar kasashen nahiyar Afrika AG ta nuna cewa, kasashen Afrika suna fatan kasashe masu wadata za su samarwa kasashen Afrika dala biliyan 500 zuwa 600 domin taimaka musu wajen tinkarar batun sauyin yanayi.

Kakakin kungiyar ya yi kira ga taron Durban da ya kaddamar da asusun neman taimako game da batun yanayi na GCF domin ba da gudumuwa ga kasashe masu tasowa wajen samun kudin tinkarar batun sauyin yanayi.

Taron Cancun da aka yi a shekarar 2010 ya yanke shawara cewa, kasashe masu wadata su samar da kudi dala biliyan 100 a ko wace shekara daga shekarar 2013 zuwa 2020, amma duk da haka wannan ba zai biya bukatun wadannan kasashe ba.

Kungiyar AG na kunshe da kasashe 54, wadda ta zama muhimmiyar kungiya cikin shawarwarin sauyin yanayi. A ganin kungiyar, nahiyar Afrika ya fi fama da batun sauyin yanayi. Bisa kididdigar da wasu hukumomin MDD suka bayar, an ce, ya zuwa shekarar 2020, yawan mutanen nahiyar Afrika da za su yi fama da karancin ruwan sha zai kai miliyan 7.5 zuwa miliyan 25, kuma yawan hatsi da wasu kasashen Afrika za su samar zai ragu da kashi 50 bisa 100.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China