in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta nanata goyon bayanta ga kasashe masu tasowa kan bukatunsu da ke shafar batun sauyin yanayi
2011-11-29 21:17:19 cri
Mataimakin shugaban kwamitin kula da harkokin raya kasa da gyare-gyare na kasar Sin, Mr.Xie Zhenhua a ranar 29 ga wata ya bayyana a nan birnin Beijing cewa, kasashe masu tasowa ba kawai sun kasance wadanda ke dandana illar sauyin yanayi ba, hatta ma kasashe ne da ke kokarin daukar matakai, kuma kasar Sin za ta ci gaba da nuna goyon baya ga kasashe masu tasowa bisa ga bukatunsu da ke shafar matsalar sauyin yanayi.

Xie Zhenhua ya yi wannan kalami ne a yayin bikin fara wani kwas da kasar Sin ta shirya wa kasashe masu tasowa domin tinkarar matsalar sauyin yanayi, kuma a cewarsa, kasar ta Sin za ta samar da taimako ga kasashe masu tasowa ta fannonin manyan ayyuka, fasahohin da za su yi tasiri kan matsalar sauyin yanayi, fasahohin yin tsimin makamashi da na sarrafa kayayyaki ta amfani da makamashin da za a iya sabuntawa, kana da inganta kwarewarsu.

Jami'ai sama da 60 da suka fito daga wasu kasashe sama da 30 da ke fuskantar koma bayan tattalin arziki, da wadanda ke kasancewa a kananan tsibirai da kuma nahiyar Afirka sun halarci kwas din.

A yayin da yake bayani kan taron da ake yi a Durban, Xie Zhenhua ya ce, Sin za ta ci gaba da taka rawar gani, kuma za ta kara daidaitawa da sauran kasashe, a kokarin neman cimma sakamako mai kyau a wajen taron.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China