in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron COP17/CMP7 a Durban
2011-11-28 20:49:38 cri
Ranar 28 ga wata, a birnin Durban dake bakin tekun kasar Afirka ta Kudu, an bude taron bangarori masu ruwa da tsaki kan yarjejeniyar shawo kan matsalar sauyin yanayi ta MDD karo na 17 (COP17) kuma taron bangarorin da suka daddale yarjejeniyar Kyoto karo na 7 (CMP7).

A cewar Christiana Figuere, sakatriyar zartaswa ta hukuma mai kula da yarjejeniyar shawo kan matsalar sauyin yanayi ta MDD, burin da ake neman cimmawa a wannan taro shi ne tsawaita wa'adin yarjejeniyar Kyoto, da kiyaye wani tsari na bin yarjeniyoyi 2 wajen kokarin tinkarar sauyawar yanayi.

A nasu bangare, Kasar Sin, India, Brazil da Afirka ta Kudu, wadanda ke halartar taron COP17/CMP7 a matsayin wakilan kasashe dake tasowa, sun jaddada cewa, yarjejeniyar Kyoto ta kasance tushe na shawarwarin MDD kan batun sauyin yanayi, kana ya kamata a ba da fifiko ga aikin tabbatar da wa'adi na 2 na yarjejeniyar don ci gaba da kokarin cika alkawarin da aka dauka.

Wa'adin farko na yarjejeniyar Kyoto, wadda aka kulla a shekarar 1997, zai cika a shekarar 2012. Sakamakon yadda wasu kasashe masu sukuni suka ki amincewa da wa'adi na 2 na yarjejeniyar, shi ya sa ake sanya ayar tambaya kan shin ko za a iya tsawaita wa'adi na yarjejeniyar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China