in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Abubawan da suka faru kwanan nan ya bada babbar dama na samu daidaituwan sha'anin tsaro a Somalia inji AU
2011-11-21 15:17:12 cri
Kamfanin dillanci labaru na kasar Sin Xinhua ya bada labarin cewa kwamitin tsaro da zaman lafiya na kungiyar tarayyar kasashen Africa,AU yace al'amurran da suka faru a kwanan nan a Somalia,musammam ma tilasta ma janyewar kungiyar yan adawa da gwamnati na al Shabab daga Mogadishu da kuma aikin da Kasar Kenya take yi na yakan su ya bada wata dama mai kyau da za'a daidaita sha'anin tsaro a cikin Somalia.

A cikin wata sanarwar da kwamitin ta raba ma 'yan jaridu lahadin nan,tace wannan dama ya kuma taimaka wajen karfafa kokarin da ake yi wajen inganta bude wata hanya na aiwatar da siyasa kamar yadda masu ruwa da tsaki suka tsara a birnin na Mogadishu a farkon watan satumban wannan shekara a matsayin shawaran da ya biyo bayan yarjejeniyar Kamfala a watan Juni da ya gabata.

Kwamitin a taronsa na 298 da aka yi ranar 17 ga wannan watan ya samu bayani game da halin da ake ciki a Somalia daga wajen kwamishinan zaman lafiya da sha'anin tsaro,wakilin gwamnatin rikon kwarya na kasar Somalia da kuma Kasar Habasha,har ma da Shugaban gamayar gwamnatoci ta fannin cigaba IGAD da kuma tarayyar kasashen larabawa da MDD.

Kwamitin ta yaba ma gwamantin rikon kwarya na Somaliya da kuma rundunar Kungiyar Tarayyar Kasashen Africa dangane da juriya da sadaukar da kai da suka yi sannan kuma ta sake mika babban yabo ga wadanda suka rasa rayukan su ko suka raunana a wajen wannan kokari na tabbatar da an samu biyan bukata.

Sanarwar tace kwamitin na kara jaddada yabawarta ga gwamnatocin kasashen Burundi da Uganda domin taimaka ma dawo da zaman lafiya da suka yi a Somalia. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China