in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumomin kasar Kamaru zasu rage da rabi harajin kwastan bisa gurbataccen man fetur da kasar take shigo da shi a shekarar 2012
2011-11-21 14:59:10 cri

Harajin kwsatan kan gurbataccen man fetur da kasar take shigo da shi da ba na asalin kungiyar tattalin arziki da kudi a kasashen dake tsakiyar Afrika (CEMAC) ba a kasar Kamaru zai ragu da rabin kashi a shekarar 2012, daga kashi 10 zuwa kashi 5 cikin 100, in ji firamanistan kasar Philemon Yang a gaban 'yan majalisar dokokin kasar a ranar Jumma'a a birnin Yaounde.

Daya daga cikin gyare gyaren da aka tsaida kan dokar kwastan, wannan mataki na nuna niyyar hukumomin kasar Kamaru na rage tallafin gwamnati ga kamfanin tatar mai na SONARA domin taimakawa farashin man fetur a gidajen shan mai in ji shugaban gwamnatin kasar a yayin da yake gabatar da jadawalin kasar na gaba kan tattalin arziki, kudi, al'umma da kuma al'adu a zauren wakilan kasar.

Kasar Kamaru karamar kasa a wajen fitar da man fetur, tana fitar da gurbataccen man ne kawai, rashin sarrafawa a gida na sanya kasar sayar da shi kai tsaye a kasuwannin duniya, matsalar dake tilastawa wannan kasa dake tsakiyar Afrika sake odar man domin bukatunta na cikin gida daga kasashen Najeriya da Guinee Equatoriale dake makwabtaka da ita.

Yawan man fetur da kasar ke shigo da shi ya kai lita miliyan 131 a kowane wata, sannan bisa manufar tallafawa farashi a gidajen shan mai, gwamnatin kasar tana zuba kudin tallafi a kowane wata kusan biliyan 27 kudin Sefa kimanin dalar Amurka miliyan 54 in ji ministan kudin kasar mista Essimi Menye.(Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China