in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wen Jiabao ya isa birnin Saint Petersburg domin halartar taron faraministoci na kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai
2011-11-07 09:52:07 cri

Firaministan kasar Sin Wen Jiabao ya isa birnin Saint Petersburg na kasar Rasha a ran 6 ga wata da yamma, domin halartar taron firaministoci na kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai a karo na 10.

A gun taron, firaministan Sin Wen Jiabao zai takaita halin da ake ciki na ci gaban yin hadin gwiwa a tsakanin kasashen kungiyar a cikin shekarar da ta wuce tare da sauran firaministoci, kana za su tattauna kan yanayin kasa da kasa da na shiyya-shiyya da tsara fasalin hadin gwiwarsu na nan gaba a fannonin tsaro da tattalin arziki da al'ada da sauransu bisa matsayin da aka cimma a gun taron koli na Astana da aka yi a watan Yuni na wannan shekara.

An kafa kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai a shekarar 2001, wadda ta hada da kasashe 6 wato kasashen Kazakhstan da Sin da Kirghizstan da Rasha da Tadzhikistan da kuma Uzbekistan. Kana kasashen Mongolia da Pakistan da Iran da India su 'yan kallo ne na kungiyar.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China