in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 279 ne suka mutu sakamakon girgizar kasa a kasar Turkiya
2011-10-25 13:57:55 cri

Ranar Litinin 24 ga wata a birnin Ankara, kakakin gwamnatin kasar Turkiya kana mataimakin firaministan kasar ya ce, girgizar kasa mai tsanani da ya abku a lardin Van dake gabashin kasar a ran 23 ga watan, ya haddasa mutuwar mutane a kalla 279.

Ban da wannan kuma, wannan bala'in ya yi sanadiyyar abkawar gine-gine har 2200 yayin da mutane kusan 1300 suka raunana.

A game da wannan lamari, ya zuwa yanzu shugabannin kasashe ko yankuna 51 sun bugawa shugabanni da gwamnatin kasar Turkiya waya domin jajenta masu.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, kasar Turkiyan ta riga ta tura motocin agaji 450 domin aikin ceto . Kuma ya zuwa yanzu an riga an daidaita batun samar da kayayyaki da abinci da ruwan sha da ake bukata cikin gaggawa a yawancin yankunan da bala'in girgizar kasar ya shafa.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China