in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Libya ta sanar da mutuwar Gaddafi da kuma 'yantar da kasar
2011-10-21 10:22:40 cri

A ran 20 ga wata, a birnin Tripoli, wakilin kwamitin wucin gadi na kasar Libya Abdulrahim Rahimah ya sanar da cewa, a ran 22 ga wata, a birnin Banghazi, gwamnatin kasar Libiya za ta gabatar da sanarwar 'yantar da kasar.

Abdulrahim Rahimah ya kara da cewa, bayan da aka gabatar da sanarwar, galibin wakilan kwamitin wucin gadi na kasar Libya za su isa birnin Tripoli. Bisa labarin da shugaban kwamitin gudanarwar kwamitin wucin gadi na kasar Libya Mahmou Jibril ya bayar, an ce, gwamnatin da ke kan mulkin kasar za ta yi shawarwari kan batun kafa sabuwar gwamnatin wucin gadi bayan da aka gabatar da sanarwar.

A wannan rana, hukumar ICPO ta bayar da wata sanarwa, inda aka bayyana cewa, bayan kungiyar da kotun ICC sun tabbatar da labarin mutuwar Gaddafi, sun yi kira ga Seif al-Islam Qaddafi da ya mika kansa.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China