in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
"Tsohon shugaban kasar Libya Gaddafi ya rasu sakamakon jin rauni mai tsanani", in ji hafsan sojojin kwamitin NTC
2011-10-20 21:02:46 cri
A ranar 20 ga wata, bisa labarin da aka bayar, an ce, wani babban kwamandan dakarun kwamintin mulkin wucin gadin Libya NTC ya fayyace cewa, tsohon shugaban Libya Kanar Muammar Gaddafi ya ji tsananin rauni da har ya kai ga mutuwarsa, sai dai har yanzu hukumar Libya ba ta tabbatar da wannan labari ba.

A sa'i daya kuma, wani jami'in kungiyar tsaro ta NATO ya ce, kungiyar NATO ba ta da hakkin tabbatar da da wannan labari, kuma kwamitin NTC ne ke da alhakin sanar da irin wannan labari.

Haka kuma, bisa labarin da kwamandan da muka ambata ya bayar, an ce, an kame Gaddafi a garinsa da ke birnin Sirte, kuma yayin da aka kame shi, an same shi da rauni mai tsanani a kafafuwansa, inda aka kai shi zuwa wani kebabben wuri ta jirgin sama mai saukar ungulu.

Da ma, dakarun NTC sun bayyana cewa, sun kusan mamaye birnin Sirte, kuma yanzu, suna kokarin kakkame ragowar sojoji magoya bayan shugaba Gaddafi.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China