in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Har yanzu dai dan tsohon shugaba Gaddafi yana da karfi a Bani Walid a daidai lokacin da ake ci gaba da fafatawa a garin Sirte
2011-10-20 15:05:23 cri
Mayakan kwamatin gudanarwar gwamnatin kasar Libya sun tabbatar a ranar Larabar da ta gabata cewa, sun hangi wani jerin gwanon motoci guda 30 sun nausa zuwa kudancin Bani Walid, kuma suna kyautata zaton Seif al-Islam ne dan tsohon shugaba Gaddafi tare da wasu manyan jami`an tsohuwar gwamnati.

Mai magana da yawun rundunar mayakan ta NTC mai lura da kudancin Bani Walid Mahmoud Tawfiq ya shaida wa kamfanin dillancin labaru na kasar Sin Xinhua cewa, za su ci gaba da sa ido a kan wannan ayari, sannan za su sanar da takwarorinsu dake yankin da wannan tawaga ta nufa domin daukar mataki.

A game da halin da ake ciki a Bani Walid kuwa dake da tazarar 180km kudu maso gabashin birnin Tripoli, Tawfiq ya bayyana cewa, dakarun kwamitin na NTC suna ci gaba da sintiri a sassa daban daban na birnin kuma sun samu nasarar kame a kalla sojoji 300 masu goyon bayan Gaddafi tare da makamansu.(BAGWAI)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China