in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Angola ya jaddada cewar ayyukan tabbatar da zaman lafiya da yin hadin gwiwa da samun bunkasa su ne manyan manufofin da kasar za ta dauka cikin dogon lokaci
2011-10-19 10:53:20 cri
Shugaban kasar Angola Dos Santos ya ce ayyukan kiyaye zaman lafiya a duniya tare da tabbatar da zaman lafiya a duniya da tabbatar da bunkasa tattalin arzikin cikin hali mai dorewa kasar cikin dogon lokaci a gida su ne manyan manufofin da gwamnatin sa za ta dauka.

Dos Santos wanda ya bayyana hakan a jawabin sa na shekara shekara ranar 18 ga wata ya ce, kasar Angola tana bin ka'idar warware rikice-rikice a duniya ta hanyar yin shawarwari, kuma tana adawa da warware batutuwan duniya ta hanyar nuna karfin tuwo.

Shugaban ya jaddada cewa, kasar Angola za ta ci gaba da tsayawa kan kiyaye mulkin kai da cikakken yankin kasar, kuma tana adawa da kasashen waje da suke sa hannu cikin harkokin cikin gidanta.

Ya ce kasar Angola za ta ci gaba da daukan nauyinta, da ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasashen duniya wajen yaki da 'yan ta'adda da haramtar da kazamin kudi da sayar da miyagun kwayoyi ta hanyar sumogal da sauransu.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China