Ranar Laraba 28 ga wata a birnin Tripoli, kakakin sojojin mahukuntan Libya Omar Bani ya ce, yanzu haka, an gano 'yaran Gaddafi biyu wato Seif Al-Islam da Mutassim, amma har yanzu ba a san inda Gaddafi yake ba.
A gun wani taron manema labaru da aka yi a birnin Tripoli, Omar Bani ya ce, yanzu, sojojin sun sami ci gaba mai kyau cikin yakin da ake yi a birnin Sirte, kuma za su cimma nasara ba da dadewa ba.
Omar Bani ya ce, yanzu, mahukunta ba su mayar da hankali kan inda Gaddafi yake boye ba, aikin da aka sa gaba shi ne 'yantar da dukkan yankunan Libya tare da tabbatar da zaman lafiyar biranen da suka 'yantar. Daga baya, shine za su yi kokarin cafke Gaddafi. A Ko wane yankin iyakar kasa da Gaddafi ya ke boye, mahukunta za su kama shi.(Amina)