in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An zabi wasu tsare tsaren ayyuka guda ukku a yayin wani taron kasa da kasa game da harkokin internet a kasar Congo-Brazzaville
2011-09-20 10:45:04 cri
Wasu muhimman tsare tsaren ayyuka guda ukku sun sami amincewa a ranar Lahadi a birnin Brazzaville na kasar Congo bayan an kawo karshen taron kasa da kasa a nahiyar Afrika kan harkokin internet musamman ma a fuskar sha'anin sabbin fasahohin zamani da sadarwa wato NTIC bisa 'yan takara 16 wadanda dukkansu 'yan asalin kasar Congo-Braza ne.

Wadannan tsare tsaren ayyukan ukku, na farko ya kasance "kafa wani shafin internet na matasa" da Aristide Cyriaque Ndiele ya gabatar, tsarin "SIG" na Patrick Harry Bouetou Kadilamio da kuma tsarin "Yvon Sita" da ba'a bada sunan wanda ya gabatar da shi ba da ya janyo hankalin kamfanin VMK, wata kungiyar wannan taro da ta samar da wasu fasahohi ga kowane daga cikinsu.

Babban dandalin musanya tsakanin kasashen Afrika na da manufar karawa juna sani, yin amfani da sabbin kayayyakin harkokin sadarwa da fasaha, haka dandalin kasa da kasa ya taimaka wajen gabatar da kasidu daban daban game da sadarwa da suka hada da " Jaridu a kan internet a Afrika", "yunkurin samar da muhimman abubuwa duk da rashin hanya mai fa'ida ga tattalin arziki mai nagarta", "karshen zamanin wayoyin karkashin kasa na 'fibre optique'", da kuma "jaridun gargajiya a wannan zamani".

Dandalin kasa da kasa kan harkokin internet a nahiyar Afrika karo na biyu zai gudana a shekarar 2012 a babban birnin kasar ta Congo Brazzaville, a cewar masu shirya wannan taro. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China