in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taron wakilan musulmi na kasar Sin karo na 9
2011-09-15 20:32:58 cri
A ran 15 ga wata, a birnin Beijing, an kammala taron wakilan musulmi na kasar Sin karo na 9 na tsawon kwanaki 3. A gun taron, an zabi sabbin shugabannin kungiyar kula da harkokin musulunci ta kasar Sin da ke karkarshin jagorancin shugaban kungiyar Chen Guangyuan.

Taron da aka shirya a wannan rana, an gabatar da ayyukan kungiyar musulmi kula da harkokin musulunci za ta yi a cikin shekaru 5 masu zuwa, Mahalartar taron sun nuna cewar ya kamata a ba da gudumawa a fannonin kiyaye zaman jituwa a tsakanin mabiyar addinai, da hadin kan kabilun kasar Sin, da tabbatar da zaman lafiyar al'ummar kasar, da kuma sa kaimi ga bunkasa tattalin arzikin kasar.

An kafa kungiyar kula da musulunci ta kasar Sin a shekarar 1953, kuma ita ce kungiyar kula da musulunci ta farko a tarihin kasar.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China