in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kashe jagoran kungiyar Al Qaeda na biyu, in ji wani jami'in Amurka
2011-08-28 17:05:32 cri
Ranar Asabar 27 ga wata, wani babban jami'in gwamnatin kasar Amurka ya ce, a ranar 22 ga wata, a Pakistan, sojojin Amurka sun kashe Atiyah ABD Al-Rahman, jagoran kungiyar Al Qaeda na biyu.

Wannan jami'in da ba ya son bayyana sunansa ya ce, an kashe Rahman ne a Waziristan dake arewa maso yammacin Pakistan, amma bai yi karin bayani ba dangane da rasuwarsa.

A baya akwai rahotannin dake nuna cewa, wani jirgin saman hukumar leken asirin Amurka wanda ba matuki a cikinsa ya kai hari a wannan wuri. Kawo yanzu dai ba'a san ko akwai wata alaka tsakanin mutuwar Rahman da wannan hari ko a'a.

An ce, Atiyah ABD Al-Rahman, dan asalin kasar Libya ne, wanda ya zama jagora na biyu na kungiyar Al Qaida bayan da aka kashe Osama bin Laden, haka kuma shi ne babban na hannun daman Ayman al-Zawahiri, jagoran kungiyar Al Qaida.

A shekarar da ta gabata, akwai rahoton da ya bayyana cewa Rahman ya mutu, amma gwamnatin Amurka da kungiyar Al Qaida ba su tabbatar da gaskiyar rahoton ba.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China