in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ce za ta yanke shawarar irin sakamakon da taron shugabannin kasashen G20 mai zuwa zai tsayar
2011-08-26 21:14:34 cri
A yammacin ranar 26 ga wata, Francois Baroin, ministan kudin kasar Faransa, wanda ke cikin tawagar shugaban kasar Nicolas Sarkozy a ziyararsa a birnin Beijing na kasar Sin, ya bayyana cewa, matsayin kasar Sin da rawar da take takawa ne za su tabbatar da irin sakamakon da za a iya samu a yayin taron shugabannin kasashen G20 a karo mai zuwa.

A kwanaki 2 da suka gabata, Mista Baroin ya gana da Wang Qishan, mataimakin firaministan kasar Sin, da Xie Xuren, ministan kudi na kasar, gami da sauran wasu manyan jami'an Sin ta fuskar harkokin kudi, inda bangarorin 2 suka yi musayar ra'ayoyi kan yanayin da tattalin arzikin duniya ke ciki, batutuwan da za a tattauna a taron shugabannin G20 da zai gudana a watan Nuwamba, yadda za a gyara tsarin kudi na kasa da kasa, da rikicin bashi da kasashen Turai suke fama da shi. Ban da haka kuma, bangaren Faransa ya yi bayani filla-filla kan yadda kasashen Turai suke kokarin shawo kan matsalar tattalin arziki a kasar Girka. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China