in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana ci gaba da fafatawa a wasu wurare na birnin Tripoli
2011-08-25 16:38:25 cri

A ran 25 ga wata, dakaru masu adawa da gwamnatin kasar Libya da sojojin gwamnatin kasar suna ci gaba da yin yaki a wasu wuraren birnin Tripoli. Wasu dakaru sun shiga yankin Soult, tsohon mazaunin Muammer Gaddafi don ci gaba da gudanar da aikin soja.

A wannan rana, an gwabza yaki a wasu wurare da ke birnin Tripoli a tsakanin dakaru masu adawa da gwamnatin kasar Libya da sojojin gwamnatin kasar. Dakaru sun kafa wuraren tsinkaya a dukkan mararraban hanyoyi na birnin, don duba motocin dake kai da kawowa. A ran 24 ga wata, shugaban kwamitin wucin gadi na kasar Mustafa Abdul Jallil ya bayyana cewa, yawan mutanen da suka mutu a sakamkon yakin da aka yi a Tripoli ya kai a kalla 400, kuma mutane 2000 sun ji rauni.

A ran 24 ga wata, kakakin dakaru masu adawa da gwamnatin Ahmad Barney ya bayyanawa manema labaru cewa, mai yiyuwa ne Muammer Gaddafi yana zaune a yankin hamada da ke tsakanin yankin kudancin Soult da birnin Sabah. Yanzu, sojojin da ke karkarshin jagorancin Muammer Gaddafi suna ci gaba da mallaka yankin Soult da birnin Sabah.

A wannan rana, shugaban kasar Faransa Nicolas Sarkozy ya sanar da cewa, za a shirya wani taro kan halin da kasar Libya take ciki a ran 1 ga wata mai zuwa a birnin Paris, a gun taron za a tattauna kan batun sake gina kasar Libya.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China