in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamata ya yi jama'ar kasar Libya su tsara makomar kasar da kansu
2011-08-24 10:56:38 cri

A ran 23 ga wata, ministan harkokin waje na kasar Sin Yang Jiechi ya bayyana cewa, a ganin kasar Sin, kamata ya yi a maido da zaman lafiya a kasar Libya ba tare da bata lokaci ba, kuma jama'ar kasar su tsara makomar kasar da kansu.

A wannan rana, Yang Jiechi ya buga waya ga babban sakataren MDD Ban Ki-moon game da halin da ake ciki a kasar Libya bisa tuntubar sa da aka yi , inda ya bayyana cewa, yanzu dai an shiga muhimmin lokaci a kasar Libya. Kamata ya yi bangarori daban daban na kasar Libyan su kaddamar da aikin siyasa na hadin gwiwa, da samun daidaito don sake gina kasar ta hanyar yin shawarwari cikin lumana.

Kana Yang Jiechi ya jaddada cewa, ya kamata a tabbatar da tsaron hukumomin harkokin waje na kasa da kasa dake kasar Libya tare da ma'aikatansu, yana fatan MDD za ta taka muhimmiyar rawa kan wannan batu.

Ban Ki-moon ya ce, MDD zata taka muhimmiyar rawa wajen taimakawa kasar Libya kan sake ginawa,don haka tana son yin hadin gwiwa tare da kasar Sin kan wannan batu , kuma tana son yin mu'amala tare da hukumomin yankuna da abin ya shafa.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China