in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an jam'iyyar adawa ta kasar Libya sun yi ikirari cewa, kasar Libya ta shiga wani sabon zamani
2011-08-22 15:39:29 cri

Mataimakin shugaban kwamitin wucin gadi na kasar Libya Abdel Hafis Ghoga ya furta a gidan talibijin Al-jazeera da asubahin ranar 22 ga wata cewa, Moammar Gaddafi ya taba zama tauraro a kasar Libya, amma yanzu, jama'ar kasar sun riga sun hambarar da mulkinsa, kasar Libya ta shiga wani sabon zamani.

Abdel Hafis Ghoga ya ce, za a yi babban zabe bisa tsarin mulkin kasar na wucin gadi, yana fatan za a kafa wata kasa ta dimokuradiyya na fararen hula, wannan shi ne burin jama'ar kasar Libya.

Wani wakilin kwamitin wucin gadi na kasar Libya ya bayyana a ran 22 ga wata cewa, jam'iyyar adawa ta riga ta mamaye birnin Tripoli, babban birnin kasar Libya, inda take neman Gaddafi ruwa a jallo, kuma tana kokarin murkushe dakarun sa.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China