in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sake samun rikici a tsakanin sojojin gwamnatin kasar Yemen da dakaru masu adawa da gwamnatin kasar a babban birnin kasar
2011-08-06 17:22:11 cri
A ran 5 ga wata, a yankin Hassaba na birnin Sana'a, hedkwatar mulkin kasar Yemen, sojojin gwamnatin kasar da dakaru masu adawa da gwamnatin kasar da ke karkashin jagorancin Sadiq Al-Ahmar sun yi musanyar wuta, wanda ya yi sanadiyyar jikkatar mutane da yawa, wannan ne karo na farko da bangarorin biyu suke sake yin musanyar wuta tun bayan da suka kulla yarjejeniyar tsagaita bude wuta a farkon watan Yuni.

Bisa labarin da wani jami'in mai kula da harkokin cikin gida na kasar Yemen ya bayar, an ce, dakaru masu adawa da gwamnatin kasar sun fara bude wuta ga sojoji da ke sintiri, alamarin da ya haddasa musanyar wuta a tsakanin bangarorin biyu, kuma sojojin gwamnatin kasar sun tura sojoji da dama zuwa yankin Hassaba.

Tun daga ran 4 ga wata da dare, an kara shiga hali mai tsanani a wannan yanki, saboda dakaru masu adawa da gwamnatin kasar sun hana wasu sojojin gwamnatin kasar shiga wannan yanki.

Bisa labarin da wadanda suka ganewa idonsu lamarin suka bayar, an ce, rikicin ya yi sanadiyyar raunanta mutane da yawa, daga cikinsu akwai fararen hula, amma babu wanda ya mutu a sakamakon rikicin.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China