in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ba a tsagaita musayar wuta cikin watan azumi ba a kasar Libya.
2011-08-04 16:27:42 cri

Daga ran 1 ga wata,aka shiga watan azumin Ramadan na addinin Musulunci, amma, sojojin gwamnatin Libya da dakarun 'yan adawa ba su dakatar da musayar wuta tsakaninsu ba.

A ran 2 ga wata da sassafe,sai da bangarorin biyu suka yi musayar wuta a Zlitan birni mafi muhimmanci dake yammacin Tripoli babban birnin kasar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 7 na kungiyar adawa yayin da wasu 50 suka raunana.

A sa'i daya kuma,an kasa samun zaman lafiya a sararin tekun Libya. A ran 3 ga wata, jirgin yaki mai dauke da makamai masu linzami da ake kira "Bersagliere" na kasar Italiya wanda ke shiga matakin sojan da NATO ta dauka da zummar kai hare-hare kan Libya, ya gamu da harin da aka kai shi.

Wani Manazarci ya lura da cewa, rikicin Libya ba zai kare a cikin gajeren lokaci ba. Game da halin da ake ciki kuwa a yanzu, ya ce, kasashen yamma na goyon bayan kungiyar adawa da zummar dakile mulkin Gaddafi, hakan ya sa kungiyar ta tanadi isasshen kudi, makamai da kayayyakin yau da kullum ta yadda za su yi gwagwarmayya cikin dogon lokaci.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China