in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Jonathan na Najeriya ya yi kira ga Musulmai na Nijeriya da su yi addu'a ga kasar
2011-08-02 20:41:58 cri
A ran 1 ga watan Agusta, Musulmai a duniya suka fara azumin watan Ramadan, a wannan rana kuma, shugaba Goodluck Jonathan na Nijeriya ya yi kira ga dukkan Musulmai a Nijeriya da su yi addu'a ga kasar ta Nijeriya, don samun zaman lafiya, da zaman karko, da kuma samun bunkasuwa a fannonin tattalin arziki da zaman al'umma.

A ranar 1 ga watan Agusta, shugaba Jonathan ya rubuta wata wasika domin taya murna ga Musulman Nijeriya na shiga watan Ramadan, wanda yake da muhimmancin gasket ga musulmai.

Jonathan ya ce, a watan Ramadan Allah ya kan amsa addu'o'in Musulmai, sabo da haka ya ce, ya kamata dukkan Musulman Nijeriya su yi amfani da wannan kyakkyawar dama, su yi addu'a ga kasar wajen samun kyakkyawar makoma.

Jonathan ya ci gaba da cewa, yana fatan Musulmai za su hada kai da sauran al'ummar kasar, ta yadda za su iya taimakawa gwamnati wajen samun bunkasuwa.(Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China