in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da wani "sansanin kasa" na matasan Nijar da Najeriya
2011-07-26 11:48:15 cri
"Sansanin kasa" karo na biyar na matasan Nijar da Najeriya an kaddamar da shi a wannan mako a garin Takeita dake nisan kilimita 50 daga yammacin birnin Damagaram dake tsakiyar kasar inda aka samu halartar matasa sama da 500, a cawar kamfanin dillancin labarai na ANP na kasar Nijar.

Wannan "sansanin kasa" na matasa da a shekarun baya ake kiransa "Sahel vert" a wannan karo an masa taken "Changer notre monde", wato " mu canza duniyarmu"

A tsawon wannan haduwa ta mako daya, matasan kasashen biyu za su dasa itatuwa 7000 a wasu wuraren da aka kebe.

Ministan matasa da al'adun kasar Nijar, Hassan Kounou ya shugabanci bikin kaddamar da wannan haduwa, haka kuma ministan ya nuna cewa wannan haduwa za ta taimakawa matasan sada zumunci da yin musanyar ra'ayi kan batutuwan da suka shafi yaki da fari, wasannin motsa jiki, tsabtace muhalli, warware rikici ta hanyar sulhu da kuma batun yaki da ciwon sida. (Mamane Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China