in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Jamus ta samarwa kungiyar adawa ta kasar Libya rancen kudi Euro miliyan 100, in ji kafofin yada labaru na kasar Jamus
2011-07-25 10:43:14 cri
Ranar Lahadi 24 ga wata, wani gidan telibijin na kasar Jamus ya ba da labarin cewa, ma'aikatar harkokin waje ta kasar ta sanar da samarwa kwamitin wucin gadi na kungiyar adawa ta kasar Libya rancen kudi Euro miliyan 100.

A cikin wata sanarwa, ma'aikatar harkokin wajen kasar ta ce, gwamnatin kasar ta samarwa kungiyar adawa wadannan kudaden ne domin taimaka mata wajen kyautata zaman rayuwar jama'a da aikin ba da agaji. Sanarwa ta ce, za a yi amfani da wadannan kudade domin sake gina wasu manyan ayyukan more rayuwa da aka lalata lokacin yakin basasa da kuma samarwa jama'ar Libya jiyya da abinci.(Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China