in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Congo Kinshasa ta sanar da zaman makoki domin mutanen da suka rasu a hadarin jirgin sama
2011-07-10 20:38:46 cri
A daren ranar 9 ga wata, gwamnatin kasar Congo Kinshasa ta sanar da mutuwar mutane 72 a sanadiyyar hadarin jirgin sama da ya abku a ranar 8 ga wata a birnin Kisangani na kasar, kuma tun daga wannan rana, za a fara zaman makoki na tsawon kwanaki uku a duk fadin kasar.

A ranar 8 ga wata, wani jirgin sama samfurin Boeing 727 mallakar kamfanin Hewa Bora Airways ya yi hadari a yayin da yake kokarin sauka a filin jirgin saman birnin Kisangani. Ya zuwa yanzu, babu wani takamaiman bayani game da yawan mutanen da suka mutu a sakamakon hadarin. Jami'ai a asibitin birnin Kisangani sun ce, mutane 77 ne suka mutu, amma a cewar masu agaji na kungiyar Red Cross, gawawwaki 74 ne kawai suka gano. A sa'i daya, ma'aikatar sufuri ta kasar ta ce, hadarin ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 127, a yayin da wasu 51 suka samu damar tsira da rayukansu.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China