in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani jirgin ruwa dauke da 'yan gudun hijira na kasar Libya ya nutse a tekun kasar Tunisiya
2011-06-03 20:29:57 cri
A ranar 2 ga wata, bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na Tunisiya ya bayar, an ce, kwanan nan, wani jirgin ruwa dauke da 'yan gudun hijira na kasashen arewacin Afrika sama da 700 ya gamu da hadari, bayan da ya tashi daga kasar Libya zuwa Italiya, kuma an ceci mutane 570, kana wasu sama da 200 sun bace.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, a ranar 31 ga watan Mayu da dare, rukunin 'yan sandan teku na kasar Tunisiya ya samu labari cewa, yayin da wani jirgin ruwa dauke da 'yan gudun hijira ya kai zuwa wani wurin da ke da nisan kilomita 30 zuwa tsibirin Kerkenah, inda ya gamu da hadari, an ce, akasarin mutanen da ke cikin jirgin, 'yan kasashen Afrika ne da suka tsere daga yake-yaken kasar Libya, cikinsu har da mata da yara.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, a wannan rana, yanayi a wurin ba ya da kyau, kuma 'yan gudun hijira sun yi wa jirgin yawa, lamarin da ya jawo nutsewar jirgin. Wannan jirgin ya yi ta bin ruwa a teku har ta tsawon kwanaki 5, yayin da mutanen da ke cikin jirgin suka yi ta kokarin shawo kan barazanar igiyar ruwa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China