in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
NATO ta ci gaba da kai hare-hare ta sama kan birnin Tripoli
2011-05-18 17:25:39 cri

Ranar Talata 17 ga wata, dakarun kungiyar tsaro ta NATO sun sake yin luguden wuta ta sama kan Tripoli, babban birnin kasar Libya, haka kuma kafofin watsa labarai da dama sun tabbatar da cewa, ministan kula da harkokin man fetur na kasar Shokri Ghanem ya sauka daga mukaminsa, har ma ya tsere zuwa kasar Tunisiya. Idan wannan labari ya kasance gaskiya, hakan na iya kara raunana mulkin Gaddafi.

A wannan rana, kungiyar NATO ta sake kai hare-hare ta sama kan birnin Tripoli. Wani rahoto daga gidan telebijin na kasar Libya ya ce, jiragen saman yaki na NATO sun jefa boma-bomai kan benaye biyu na gwamnatin kasar, wadanda ke dab da wurin da Moammar Gaddafi ke zaune na barikin soja na Bab al-Azizia. Kakakin gwamnatin kasar Libya Moussa Ibrahim ya ce, a daya daga cikin benayen biyu da aka kai hare-haren, an ajiye wasu takardun bayanan cin hanci da rashawa da suka shafi wasu tsoffin jami'an gwamnati wadanda suka sauya sheka zuwa bangaren 'yan hamayyar kasar. Moussa Ibrahim ya ce, kungiyar tsaro ta NATO ta kai hare-hare ta sama ne da nufin lalata wadannan takardu.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China