in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Pakistan ta zargi Amurka da daukar matakai bisa radin kanta
2011-05-15 17:28:54 cri
A ranar 14 ga wata, majalisar dokokin Pakistan ta zartas da wani kuduri dangane da kisan jagoran kungiyar Al-Qaeda Osama Bin Laden da sojojin Amurka suka yi a kasar, inda ta zargi Amurka da daukar matakai bisa radin kanta kuma ta keta 'yancin Pakistan, kuma ta yi kira ga gwamnatin kasar da ta sake yin la'akari da yarjejeniyar da ta daddale da Amurka, don tabbatar da dacewarta da moriyar kasar.

A wannan rana, bayan da majalisar dokokin Pakistan ta saurari rahoton da babban jami'in soji na kasar ya gabatar, ta yi Allah wadai da aikin soji da Amurkawa suka yi, kuma ta yi nuni da cewa, daukar matakai bisa radin kanta da Amurka ta yi ba zai amfanawa yunkurin yaki da ta'addanci a kasashen duniya ba, haka kuma ta bukaci gwamnatin Pakistan da ta kafa wani kwamitin mai zaman kansa don bincike kan wannan lamari, don magance sake abkuwar irinsa.

A sa'i daya kuma, majalisar dokokin Pakistan ta bukaci Amurka da ta dakatar da yin amfani da jiragen sama marasa matuka don kai hare-hare a kasar. Haka kuma, a cikin kudurin, an ce, ba za a amincewa sojojin kundumbala na Amurka su kai hare-hare ga yankin Abbottabad da yin amfani da jiragen sama marasa matuka don kai hare-hare a Pakistan yadda ta ga dama ba, idan kasar Amurka ba ta dakatar da daukar matakai irin wadannan ba tamkar haka, gwamnatin Pakistan za ta yi la'akari da daukar kwararan matakai, cikinsu, har da hana taimakawa kungiyar tsaro ta NATO don kai kayayyaki zuwa Afghnistan.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China