in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci kwamitin kula da harkokin 'yancin addini na kasa da kasa na Amurka da ya dakatar da yin shisshigi kan harkokin cikin gidanta
2011-05-04 20:48:41 cri
A ranar 4 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Madam Jiang Yu ta bayyana cewa, Sin ta bukaci kwamitin kula da harkokin 'yancin addini na kasa da kasa na Amurka da ya daina nuna bambancin ra'ayi ga kasar Sin, kuma ya bi gaskiya, da dakatar da yin shisshigi kan harkokin cikin gida na kasar Sin ta hanyar ba da rahotanni.

Kwanan baya, kwamitin kula da harkokin 'yancin addini na kasa da kasa na Amurka ya ba da rahoto game da 'yancin addini na kasashen duniya na shekarar 2011, inda ya sake yin suka ga kasar Sin. A wannan rana, yayin da Madam Jiang Yu ke zantawa da manema labaru, ta ce, gwamnatin Sin ta tabbatar da 'yancin addini na jama'arta bisa dokokin kasar, kuma jama'ar kasar na da cikakken hakki wajen bin addini cikin 'yanci. Sabo da haka, Sin ta bukaci wannan kwamitin da ya daina nuna bambancin ra'ayi ga kasar Sin, kana ya dakatar da yin shisshigi ga harkokin gida na Sin ta hanyar ba da rahotanni.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China