in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gwabza fada a tsakanin sojojin Faransa da dakarun Gbagbo
2011-04-07 21:24:41 cri
Sojojin kasar Faransa da ke Cote d'Ivoire sun sake yin musanyar wuta da dakarun da ke biyayya ga Laurent Gbagbo a ranar 6 a wata a dab da fadar shugaban kasar da ke birnin Abidjan.

Sanarwar da ofishin jakadancin kasar Faransa a Cote d'Ivoire ya bayar ta yi nuni da cewa, al'amarin ya faru ne a yayin da sojojin Faransa ke kokarin dauke jakadan kasar Japan a Cote d'Ivoire, a lokacin ne suka fuskanci harbe-harbe daga dakarun Gbagbo. Daga bisani, sojojin Faransa suka mayar da martani da jirgin sama mai saukar ungulu.

Sanarwar ta kara da cewa, bisa ga yadda Japan da MDD suke bukata, sojojin Faransa sun dauke jakadan kasar Japan a Cote d'Ivoire zuwa sansaninsa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China