in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magoya-bayan Ouattara sun kai farmaki kan fadar Gbagbo
2011-04-07 11:00:35 cri

Bayan rugujewar tattaunawar da Majalisar Dinkin Duniya da kasar Faransa suka shirya don neman Laurent Gbagbo ya ba da kai, da safiyar ranar 6 ga wata, magoya-bayan Alassane Ouattara sun kai farmaki na karshe kan fadar Gbagbo dake Abidjan.

Dakarun jami'an Ouattara sun ce za su dauki matakin soja domin kama Gbagbo da ransa, a kokarin kawo karshen rikicin siyasar da aka shafe watanni da dama ana yi a kasar Cote D'ivoire.

Kakakin jami'an Laurent Gbagbo Mista Ahoua ya fadawa manema labarai cewa, an yi amfani da wasu manyan makamai don kai hare-hare kan fadar Gbagbo. Ahoua ya kuma la'anci dakarun Ouattara da kulla makarkashiyar kashe Gbagbo, haka kuma ya ce rukunin sojojin Faransa dake Cote D'ivoire na Licorne ya samar da tallafin soja ga dakarun Ouattara wajen kai farmaki kan Laurent Gbagbo.

Amma rukunin sojojin Licorne ya musunta wannan zance.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China