in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wane irin tasiri ne rikicin kasar Libya zai haifar?
2011-04-05 17:06:08 cri

Tun bayan barkewar rikici a kasar Libya, an samu hauhawar farashin man fetur a duniya. Bayan haka kuma, hare-haren wasu kasashen yamma da kungiyar NATO a kasar sun haddasa karin farashin man fetur. An kimanta cewa, a wannan yanayi na rikici da ake ciki, za a ci gaba da samun karuwar farashin man fetur, har ma ana ganin zai kai dalar Amurka 150 a ko wace ganga a karshen shekarar da muke ciki. A waje guda kuma, a kasar Japan za a soma aiwatar da ayyukan sake raya kasar bayan bala'in girgizar kasa, inda za ta bukaci man fetur da yawa, shi ne kuma wani muhimmin dalili na daban da zai kara farashin man fetur. Wane irin tasiri ne farashin man fetur na duniya zai kawowa tattalin arzikin duniya sakamakon wadannan manyan lamuran biyu? Wannan ya zama wani batun dake jawo hankalin kasashen duniya.

Gaskiya ne, tashe-tashen hankulan da aka samu a gabas ta tsakiya da arewacin kasashen Afrika, da kuma ayyukan sake raya kasar Japan bayan bala'in girgizar kasa za su kara farashin man fetur na duniya, kana za su yi mugun tasiri ga farfadowar tattalin arzikin duniya, musamman ma ga kasashen Turai. Yanzu kasashen Turai na fuskantar yawan basussuka, tun fil azal kasashen dake arewacin Afrika na samar da man fetur ga kasashen Turai. Saboda haka, idan kasashen dake arewacin Afrika ba su iya samar da isashen man fetur ba, to dole ne kasashen Turai su nemi man fetur daga wasu kasashe masu nisa, wannan zai janyo musu kara biyan kudin jigila, wanda zai yi tasiri ga samar da kayayyaki da kuma sayen kayayyaki. Bugu da kari, karuwar farashin man fetur za ta yi babban tasiri ga kasashen da ke dogara kan shigar da man fetur, ciki har da kasar Japan.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China