in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen yamma sun fara kai hare-hare kan sojojin kasa na Libya
2011-03-25 17:00:00 cri

Ranar 24 ga wata, rana ce ta shida da kasashen yamma suka dauki matakan soja kan kasar Libya, amma abu sabo shi ne jiragen saman yaki na kasashen yamma sun fara mai da hankali kan kai wa sojojin kasa na Libya hare-hare a maimakon sojojin sama kawai. A waje daya kuma, kasar Amurka ta bayyana aniyarta ta sakin ragamar ba da umurni ga wannan aikin soja, yanzu dai kasa da kasa na ta mai da hankali kan batun. To yanzu ga cikakken bayani.

A ran 24 ga wata, kasashen yamma sun ci gaba da kai wa kasar Libya hare-hare ta sama, an sake jin amon fashewar boma-bomai a birnin Tripoli, babban birnin kasar Libya da kuma yankunan da ke kewayensa. A ranar kuma, kasar Faransa ta harbi wani jirgin saman yaki na kasar Libya a sararin sama na birnin Misrata da ke da nisan kimanin kilomita 200 daga birnin Tripoli. Greg Bagwell, mataimakin babban kwamandan sojojin sama na kasar Birtaniya ya bayyana kwanan nan cewa, bayan da ake ta kai hare-hare ta sama har na tsawon kwanaki da dama, an riga an raunana karfin sojan kasar Libya a sararin sama. Haka kuma sakamakon kafuwar yankin hana shawagin jiragen sama, kasashen yamma sun fara mai da hankali kan kai wa sojojin kasa na Libya farmaki ta hanyar amfani da jiragen saman yaki, tare da burin raunana sojojin gwamnatin kasar Libya da ke fafatawa da dakaru masu adawa. Kafofin watsa labaru na kasar Amurka sun ba da labari a wannan rana, cewar wannan canji ya sheda cewa, aikin soja da ake gudanar kan kasar Libya ya shiga mataki na biyu.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China