in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen yamma suna ci gaba da kai wa kasar Libya hare-hare
2011-03-24 17:14:04 cri

A ran 23 ga wata, kasashen yamma sun ci gaba da daukar matakan soja ga kasar Libya, sojojinsu sun kara kai wa Tripoli, babban birnin kasar Libya hare-hare na sama a wannan rana. A waje daya kuma, sojojin gwamnatin kasar Libya na ci gaba da fafatawa da dakaru masu adawa da gwamnatin.

A ran 23 ga wata, kasar Amurka ta tura jiragen ruwan yaki uku zuwa Bahar Rum don sa hannu cikin aikin soja a kasar Libya. A wannan rana kuma, jiragen ruwan yaki na kungiyar NATO sun fara yin sintiri a bakin tekun da ke kusa da kasar Libya domin aiwatar da kudurin MDD kan hana Libya sufurin makamai. An labarta cewa, kawo yanzu dai kungiyar NATO ta riga ta tattara jiragen ruwan yaki 16 da kasashe shida suka samar, domin gudanar da ayyukan hana Libya sufurin makamai.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China