A ran 25 ga wata, a kasar Habasha, kungiyar AU za ta kira wani taro don tattauna matsalar Libya, wakilan kasashen dindindin na kwamitin sulhu na M.D.D da na kungiyar tarayyar kasashen Larabawa da na kungiyar EU da kasashen Brazil da India za su halarci taron.
A ran 23 ga wata, ministan harkokin waje na kasar Ghana Alhaji Muhammad Mumuni ya bayyana cewa, kasar Ghana tana nuna goyon baya ga jama'ar Libya, kuma tana son kiyaye hakkin jama'ar Libya.(Abubakar)