in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan warware rikicin kasar Libya ta hanyar yin shawarwari
2011-03-22 20:36:27 cri

A gun taron manema labaru da aka yi a ranar 22 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Jiang Yu ta bayyana cewa, kasar Sin tana adawa da haddasa mutuwar mutane ko jikkata su ko jawo babbar masifa ga kasar Libya ta hanyar yin amfani da makamai, kuma kasar Sin tana fatan warware rikicin kasar Libya ta hanyar yin shawarwari cikin lumana.

Haka kuma, Madam Jiang Yu ta ce, makasudin kudurin M.D.D shi ne tabbatar da tsaron jama'ar kasar Libya, sabo da haka Sin tana kira ga bangarorin da abin ya shafa da su tsagaita bude wuta nan take, kuma a warware batun kasar Libya cikin lumana. Haka kuma, kasar Sin tana goyon baya ga manzon musamman na sakatare janar na M.D.D da kungiyar AU da kawancen kasashen Larabawa da su yi kokari ta hanyar diplomasiyya don warware wannan batu.

Ban da wannan kuma, sabo da kwamitin sulhu na M.D.D na gudanar da shawarwari kan bukatar kasar Libya ta kira wani taron gaggawa, wasu manema labaru sun tambayi Madam Jiang Yu game da ra'ayin kasar Sin a matsayinta na kasar da ke shugabancin karba-karba na kwamitin sulhu na M.D.D na wannan wata.

A game da haka, Jiang Yu ta bayyana cewa, a matsayinta na shugabar karba-karbar kwamitin sulhu na M.D.D, Sin ta kan sauke nauyin dake kanta cikin adalci, kuma a bayyane. Zuwa yanzu, kwamitin sulhu na M.D.D na ci gaba da yin shawarwari dangane da bukatar kasar Libya, haka kuma bangarori daban daban na kwamitin za su tsaida kuduri game da matakan da za a dauka.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China