in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Libya ta fara bayar da makamai ga jama'arta
2011-03-21 10:25:48 cri

Bayan da wasu kasashen yammacin duniya suka fara kai hare-hare ga kasar Libya, kasa da kasa sun nuna bambancin ra'ayoyi game da wannan batu.

A ran 20 ga wata, gwamnatin kasar Libya ta fara bayar da makamai ga jama'arta, jama'a da dama sun taru a wurin Mouammer al Gaddafi, sun bayyana cewa, za su tabbatar da tsaron kasar da kuma na Gaddafi.

A wannan rana, kungiyar kawancen kasashen Larabawa ta yi tir da hare-haren da kasashen yammacin duniya suka kai wa kasar Libya.

Kana kasar Rasha ta yi kira ga kasashen Amurka da Ingila da Faransa da su dakatar da kai hare-hare ga kasar Libya. Kuma ma'aikatar harkokin waje ta kasar Indiya ta bayar da wata sanarwa, inda ta nuna takaici ga hare-haren da aka kai wa kasar Libya.

A wannan rana, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Iran ya bayyana cewa, kasarsa ta yi Allah wadai da hare-haren da kasashen yammacin duniya suka kai wa kasar Libya.

Amma wasu kasashe sun nuna goyon baya ga kai hare-hare a kasar Libya. Bayan da aka kai hare-haren, kasashen Australia da New Zealand da Italy da Czech da Belgium da kuma Turkiya sun nuna goyon baya ga kasashen Amurka da Ingila da Faransa da suka kai hare-haren.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China