in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Faransa za ta kira taron koli don tattauna kan yadda za a aiwatar da kudurin MDD kan batun kasar Libya
2011-03-19 17:22:28 cri

Fadar shugaban kasar Faransa ta bayar da rahoto a ran 18 ga wata cewa, za a kira taron koli kan yadda za a aiwatar da kudurin kwamitin sulhu na MDD kan batun kasar Libya a ran 19 ga wata a kasar Faransa.

An labarta cewa, shugabannin kungiyoyin duniya da kasashe da dama ciki har da babban sakataren MDD Ban Ki-moon, da babban sakataren kawancen kasashen Larabawa Amr Mahmoud Moussa, da Herman Van Rompuy, shugaban din din din na kwamitin kula da harkokin kungiyar EU, da Madam Catherine Ashton, babbar wakiliyar kungiyar EU ta fuskar manufofin diplomasiyya da tsaro, da firaminsitan kasar Birtaniya David Cameron, kana da Madam Angela Merkel, shugabar gwamnatin kasar Jamus za su halarci taron, inda za su tattauna kan yadda za a aiwatar da kudurin da kwamitin sulhu na MDD ya zartas a ran 17 ga wata kan halin da kasar Libya ke ciki.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China