in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta cimma buri na ba da jiyya ga manoma a kauyuka
2011-03-10 16:24:59 cri

A ran 9 ga wata da yamma, taron majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya shirya taron manema labaru, wanda babban jigonsa shi ne "inganta tsarin kiwon lafiya". Ministan kiwon lafiya na kasar Sin Chen Zhu ya bayyana cewa, muhimmin aiki na yin gyare-gyaren tsarin kiwon lafiya a kauyuka na kasar Sin da za a yi a bana shi ne, giggina asibitoci a gundumomi daban daban.

Game da wahalhalun da ake fuskanta, Chen Zhu ya kara da cewa, a bana, ya kamata a samarwa jama'ar kasar sauki wajen ganin likitoci.

Mataimakin darektan kwamitin kula da bunkasuwa da yin gyare-gyare na kasar Sin kuma darektan ofishin al'amuran gyare-gyaren tsarin kiwon lafiya na majalisar gudanarwa ta kasar Sun Zhigang ya bayyana cewa, a bana, za a kara inganta tsarin kiwon lafiya a kauyuka.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China