in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu wakilan majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama'ar kasar Sin sun yi kira ga kara zuba jari ga al'ummar kasar
2011-03-09 14:55:19 cri

A ran 9 ga wata, a birnin Beijing, an bude taro na 3 na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama'ar kasar Sin a karo na 11. Wakilai 16 na majalisar sun yi jawabi a gun taron, inda suka yi kira ga kara zuba jari ga al'ummar kasar da kuma kara kyautata ingancin abinci.

Shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama'ar kasar Sin Jia Qinglin ya halarci taron, a cikin jawabin da wasu wakilan majalisar da suka hada da wakilin Zhang Daning suka bayar, an ce, a 'yan shekaru da suka wuce, ba a samu ci gaba cikin sauri ba a fannin bunkasa harkokin al'ummar kasar. Ya kamata hukumomi daban daban su kara zuba jari ga harkokin al'ummar kasar, da kyautata tsarin samar da hidima ga al'ummar da kyautata tsarin kiwon lafiya da tsarin ciyar da tsoffi da taimakawa 'yan mata masu ciki da manoma  da suka rasa gonaki. Da kara kyautata ingancin abinci, don kara samar da moriya ga jama'ar kasar.(Abubakar)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China