in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jihar Ningxia za ta kara mu'amala da hadin gwiwa da kasashen musulmi
2011-03-08 20:20:58 cri

Wang Zhengwei, shugaban jihar Ningxia mai cin gashin kanta ta kabilar Hui ta kasar Sin kuma dan majalisar wakilan jama'ar kasar, ya bayyana a ranar 8 ga wata a nan birnin Beijing cewa, jihar za ta kara mu'amala da hadin gwiwa da kasashen musulmi a yayin da ake gudanar da shiri na 12 na shekaru biyar-biyar kan bunkasa tattalin arziki da zaman al'umma a kasar Sin.

A yayin da yake halartar taron shekara shekara na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin da ake yi yanzu a nan birnin Beijing, Wang ya ce, jihar ta Ningxia za ta yi kokarin gudanar da taron dandalin tattaunawar harkokin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da kasashen Larabawa yadda ya kamata, kuma za ta yi kokarin zama wani muhimmin bigire na samar da abincin halal da kayayyakin musulmi a kasar Sin kana wani babban dandali na gudanar da hadin gwiwa tsakanin kasar da kasashen musulmi.

A cewarsa, ko ta fannin tarihi da al'adu ko kuma ta fannin masana'antu, jihar Ningxia tana da fifiko wajen gudanar da hadin gwiwa da kasashen musulmi, abin da ya aza harsashi mai inganci ga inganta hadin gwiwa tsakaninta da wadannan kasashen.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China