in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta duba yiwuwar karin kudin albashi a mataki mataki
2011-03-08 16:59:05 cri

A ran 8 ga wata, ministan kula da harkokin kwadago da bada tabbaci ga zamantakewar al'umma na kasar Sin Yin Weimin ya bayyana cewa, yayin da ake gudanar da shiri na 12 na shekaru 5 na raya kasa, za ta duba yiwuwar karin kudin albashi a mataki mataki, kana za a bullo da tsarin karin kudin albashi a ma'aikatu cikin hanzari.

Yin Weimin ya bayyana cewa, a bana larduna da birane da dama za su ci gaba da duba yiwuwar karin kudin albashi. Gwamnatin kasar Sin za ta tsara ma'aunin bisa bunkasuwar tattalin arzikinta, da karuwar farashin kaya, da kuma karuwar karfin masana'antu wajen kawo albarka.

Yin Weimin ya kara da cewa, za a kafa tsarin ba da tabbaci ga al'umma da zai shafi dukkan birane da kauyuka a lokacin da ake gudanar da shiri na 12 na neman samun bunkasuwa a shekaru biyar masu zuwa, kana kafa tsarin kudin fensho na mazauna birane zai kasance mafi muhimmanci. A sa'i daya kuma, ya kamata a kara ba da tabbaci ga manoma 'yan cin rani da kuma sauran mutanen da ba su da dawamammen aikin yi.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China