in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata nauyin da kasar Sin ke dauka ya dace da halin da kasar ke ciki
2011-03-08 16:50:40 cri

Ranar 7 ga wata, a wajen wani taron manema labarai da aka shirya a Beijing, ministan harkokin wajen kasar Sin Yang Jiechi ya bayyana cewa, kasar Sin kasa ce dake tasowa, kuma tana iya taka rawa gwargwadon karfinta. Hakan na nufin cewa, ko da yake kasar Sin ta kasance ta biyu a fannin tattalin arziki a duniya, amma ita ba wata kasa ce mai karfi ba, kuma tana fuskantar wahalhalu da matsaloli da dama a yayin da take kokarin neman ci gaba, don haka kamata yayi nauyin da kasar Sin ke dauka ya dace da halin da ake ciki a kasar.

Kwanan baya, kafofin watsa labaran duniya sun ruwaito wani labarin dake cewa, kasar Sin ta kasance ta biyu a fannin tattalin arziki a duniya bayan da ta wuce kasar Japan, shi ya sa ake ganin wai ya kamata kasar Sin ta kara daukar nauyin dake kanta.

1 2 3
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China