A gun taron manema labaru da aka yi a birnin Beijing, Yang Jiechi ya ce, shugabannin kasashen Sin da Amurka sun cimma daidaito kan yadda za a inganta hadin gwiwa dake tsakaninsu. Kamata ya yi a gudanar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka tsara don inganta dangantakar abokantaka dake tsakaninsu. Ban da wannan kuma, ya bayyana cewa, akwai wasu bambancin ra'ayoyi kan wasu batutuwa a tsakanin Sin da Amurka, duk da haka, ya kamata kasashen biyu su girmama juna da warware matsalolin dake tsakaninsu yadda ya kamata.(Zainab)